Tag Archives: HUDUBA DAGA MASJIDU TAUHEED

Girman Annabi (S.A.W)

بسم الله الرحمان الرحيم.
Duk da dai Allah bai bani daman isa masallaci akan lokaci ba, ga dan kadan daga abinda na tsakuro mana…

Na shigo malam yana kan magana akan girmama annabi(صلى الله عليه وسلم‏)‏
Annabi shine fiyayye aduk cikin halittun Allah baki daya, dolene ga duk musulmi yayi koyi dashi acikin duka lamuransa…. Yaci gaba da bayani har ya gangaro kan yahud da nasara, yace bai dace ace musulmi yayi koyi dasu ba ta ko wata hanya, haka kuma bashi yiwuwa mutum ya sosu. Acikin zancensa sai ya kawo fadin Allah(subhanahu wa ta’ala) acikin suratu baqara ayah ta 120
وَلَنْ تَرْضَى عَنْكَ الْيَهُودُ ولَا النَّصَارَى حَتَّى تَتَّبِعَ مِلَّتَهُم قُلْ إِنَّ هُدَى اللَّهِ هُوَ الْهُدَى وَلَئِنِ اتَّبَعْتَ أَهْوَا ءهُمْ بَعْدَ الَّذِي جَاءَكَ مِنَ الْعِلْمِ مَا لَكَ مِنَ اللَّهِ مِنْ وَلِيٍّ وَلَا نَصِيرٍ Continue reading →