Category Archives: ZABEN 2015

Tirka-tirkar mulki a Najeriya: Idan kunne ya ji…

Da sunan Allah Mai rahama Mai jinkai.
Duk da dai Hausawa sun ce ba a shedar dan kuturu har sai ya girma da yatsunsa, amma wannan karo na shaide shi tun bai hada shekara ba. Shi ma saboda wata maganar Bahaushen mai cewa, kyakkyawar safiya tun daga marecenta ake ganewa kuma ko banza, maigirma Janar Muhammadu Buhari ya ba mu labarin cewa “Jiki magayi.” Saboda haka ina da tabbacin cewa, bari ba shegiya ba ce da ubanta; fiye da yadda na yi imani da cewa, masara idan ta ji wuta ita ke fadi. To, wane dare ne jemage bai gani ba? Continue reading →